Monday, August 10, 2026

Girgizar Ƙasa Mafi Ƙarfi Cikin Shekaru 10 Ta Hallaka Mutane 111 a Colombia.

Girgizar Ƙasa Mafi Ƙarfi Cikin Shekaru 10 Ta Hallaka Mutane 111 a Colombia.

Akalla mutane 111 ne suka rasa rayukansu, yayin da gine-gine da dama suka ruguje bayan wata girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 7.4 ta afku a yammacin ƙasar Colombia a yau Litinin.

Hukumomi sun ce girgizar ƙasar ta afku ne kusa da San José del Palmar a yankin Chocó, mai tazarar kusan kilomita 400 daga yammacin babban birnin ƙasar, Bogotá. Hukumar Binciken Ƙasa ta Amurka (USGS) ta ce girgizar ta afku ne a zurfin kusan kilomita 107.

Masu aikin ceto na ci gaba da bincike a cikin gine-ginen da suka ruguje domin gano mutanen da suka makale a ƙarƙashin baraguzan gini. 
An kuma samu mutane da dama da suka jikkata, yayin da girgizar ta tilasta wa mazauna yankuna daban-daban barin gidajensu.

Hukumar Kula da Yanayin Ƙasa ta Colombia ta bayyana girgizar a matsayin mafi ƙarfi da aka samu a ƙasar cikin shekaru 10 da suka gabata.

Shugaban Colombia, Abelardo de la Espriella, ya ayyana dokar ta-ɓaci domin a gaggauta samar da kuɗaɗen tallafin farfaɗowa daga bala'in. Ya kuma ce zai ziyarci yankunan da girgizar ta fi shafa.

Shugaban ya ce gwamnati ba za ta bar mutanen da abin ya shafa su kaɗai ba, tare da yin alkawarin cewa za a ba su dukkan taimakon da ake buƙata.

Bayan babbar girgizar ƙasar, an kuma samu wasu ƙananan girgizar ƙasa guda biyu masu ƙarfin 2.8 da 4.8.

Hukumomi sun dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a wasu filayen jiragen sama da suka haɗa da na Manizales da Quibdó da Armenia da Cartago da Buenaventura da Pereira.

A birnin Pereira, hotuna da bidiyoyin da kafafen yaɗa labarai na cikin gida suka wallafa sun nuna wani ɓangare na rufin filin jirgin sama yana faɗowa yayin da matafiya ke neman mafaka. An kuma ga mutane suna gudu a cikin wuraren da baraguzan gine-gine suka cika.

Yankin Chocó da ke bakin tekun Pacific na daga cikin yankunan da suka fi fama da talauci a Colombia. Yawancin yankunan karkara ne, kuma wasu wurare ba sa da sauƙin isa sai ta jirgin ruwa ko jirgin sama, lamarin da zai iya kawo cikas ga ayyukan ceto da tantance yawan asarar rayuka.

A babban birnin Bogotá, magajin birnin, Carlos Fernando Galán, ya ce babu rahoton mutuwar mutane ko munanan raunuka a birnin, sai dai wasu gine-gine sun samu tsagewa.

Colombia na fuskantar dubban ƙananan girgizar ƙasa a kowane wata, amma girgizar da ta kai ƙarfin maki 6.0 ko sama da haka ba kasafai take faruwa ba. 
A shekarar 1999, wata girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 6.2 ta afku a yankin noman kofi na ƙasar, inda ta hallaka sama da mutane 1,000.

Wannan bala'i ya zo ne makonni kaɗan bayan wasu manyan girgizar ƙasa sun afku a ƙasar Venezuela, inda aka ruwaito cewa fiye da mutane 6,000 sun mutu, yayin da daruruwan gine-gine suka lalace.

0 Comment about the Post: