Fadar Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu-Abubakar III, ta musanta zargin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa an taɓa hana Sarkin ganawa da tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, lokacin da yake kan mukaminsa.
A cikin wata sanarwa, fadar ta bayyana zargin a matsayin ƙarya marar tushe, tana mai cewa an ƙirƙire shi ne saboda dalilan siyasa da nufin haifar da rudani tare da ɓata sunan masarautar.
Ajiya Masu Gombe, wanda ya yi magana a madadin fadar, ya ce Mai Martaba Sarkin Gombe da Farfesa Pantami sun daɗe suna da kyakkyawar alaƙa mai cike da mutunta juna.
Ya bayyana cewa zargin da ake yi cewa an hana Sarkin ganawa da Pantami ba gaskiya ba ne, yana mai jaddada cewa bai taɓa faruwa ba a tarihin hulɗar da ke tsakanin bangarorin biyu.
Fadar ta kuma yi kira ga jama'a da su guji yaɗa labaran ƙarya ko marasa tushe da za su iya zubar da mutuncin sarakunan gargajiya.
Haka kuma, ta gargadi masu ƙoƙarin jawo masarautu cikin siyasar ɓangaranci, tana mai cewa ya kamata a mutunta martabar sarakunan gargajiya tare da nesanta su daga rigingimun siyasa.
A ƙarshe, fadar ta bayyana cewa za ta ɗauki matakin shari'a kan duk wanda aka samu yana yaɗa ƙarya ko ɓata sunan Mai Martaba Sarkin Gombe da gangan.
Ta kuma buƙaci 'yan siyasa da magoya bayansu su gudanar da harkokinsu cikin ladabi da girmama cibiyoyin gargajiya.

0 Comment about the Post: