Saturday, July 11, 2026

Jagoran Addinin Iran Ya Sha Alwashin Neman Adalci Kan Kisan Mahaifinsa.

Jagoran Addinin Iran Ya Sha Alwashin Neman Adalci Kan Kisan Mahaifinsa.

Jagoran addinin Iran, Ayatollah Mojtaba Khamenei, ya bayyana cewa neman adalci kan kisan mahaifinsa kuma tsohon Jagoran Ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei, babban buri ne na al'ummar ƙasar Iran.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Telegram a ranar Asabar, Mojtaba Khamenei ya ce al'ummar Iran na buƙatar a hukunta waɗanda ake zargi da hannu a kashe mahaifinsa, yana mai cewa wannan ba buƙatarsa kaɗai ba ce, illa ta ƙasa baki ɗaya.

Jawabin nasa ya zo ne yayin gudanar da jana'izar Ayatollah Ali Khamenei, wanda ya rasu sakamakon hare-haren sama da Amurka da Isra'ila suka kaddamar a ranar 28 ga Fabrairu.

Mojtaba Khamenei ya sake jaddada cewa Iran za ta ci gaba da neman adalci kan mutuwar mahaifinsa, yana mai cewa wannan batu ya ƙara tsananta rikicin siyasa da tsaro a yankin Gabas ta Tsakiya.

0 Comment about the Post: