Rundunar Juyin Juya Halin Musuluncin ƙasar Iran (IRGC) ta bayyana cewa ta kaddamar da wani sabon farmaki mai suna (Nasara), inda ta ce an kai harin ne kan manyan sansanonin sojin sama na Isra’ila dake Nevatim da Tel Nof, a matsayin martani ga hare-haren da Isra’ila ta kai cikin Iran.
A cikin sanarwar da rundunar jiragen sama ta IRGC ta fitar a safiyar yau Litinin, ta ce an gudanar da aikin ne da taken sirrin “Ya Haidar Karrar” tare da sadaukar da shi ga mayakan da suka yi shahada a rikice-rikicen yankin da suka gabata.
Sanarwar ta bayyana cewa an kai harin ne sakamakon abin da Iran ta kira harin makamai masu linzami na Isra’ila ta kai a wuraren da dama a cikin Iran.
Kafofin watsa labarai na Isra’ila sun ruwaito cewa an ji ƙarar fashe-fashe a sassa da dama bayan harba makaman masu linzami, inda aka ce wasu hare-haren sun sauka a kusa da birnin Haifa da sauran yankuna na arewa da tsakiyar Isra’ila.
An kuma kunna kararrawar gargadi a wurare da dama yayin da aka tashi tsarin kariya ta sararin samaniyar ƙasar.
Majiyoyin Iran sun ce makaman da aka yi amfani da su sun haɗa da nau’ikan makamai masu linzami masu matsakaici da kuma na dogon zango, tare da ikirarin cewa harin ya nuna ƙarfin shirin sojinsu da iya kai farmaki mai nisa.
Rundunar ta IRGC ta kuma yi gargadi cewa duk wani ƙarin hari daga Isra’ila zai haifar da martani mai faɗi da tsanani, wanda ka iya ƙara faɗaɗa wuraren da za a kai hari.
Hukumomin Isra’ila ba su tabbatar da cikakken barnar da aka yi ba, amma sun ce an kunna tsarin kariya da matakan gaggawa a yankunan da abin ya shafa.
Wannan musayar hare-hare na zuwa ne a yayin da rikici ke ci gaba tsakanin Iran da Isra’ila, inda kowanne bangare ke zargin ɗayan da ƙara tayar da hankali a yankin.

0 Comment about the Post: