Shugaban ƙasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce shugaban Amurka Donald Trump ba shi da wani haƙƙi na hana Iran “Mallakan nukiliya na zaman lafiya da doka ta bata”,
Inda ya jaddada cewa Iran ba ta neman faɗaɗa yaƙi, kuma tana aiki ne kawai domin kare kanta.
“Shugaban Amurka yasha fadan cewa Iran kada ta yi amfani da haƙƙin ta na nukiliya, amma ba ya bayar da amsa kan laifin da muka aikata,” in ji Pezeshkian.
“Shi wane ne shi da har zai hana wata ƙasa haƙƙin da doka ta ba ta?”
Ya kuma ƙara da cewa: “Iran ba ta neman faɗaɗa yaƙi ba, kuma ba ta fara wani rikici ba, kuma ba za ta fara ba.
Ba mu kai hari kan wata ƙasa ba, kuma a halin da ake ciki ba mu da niyyar kai hari ga kowa. Muna aiki ne kawai wajen kare kanmu bisa doka.”
A lokacin rikicin, Iran ta kai hare-hare a yankuna daban-daban, ciki har da Bahrain da Kuwait, Oman da Qatar da Hadaddiyar Daular Larabawa da Jordan da Saudi Arabia da Syria da Iraq da Turkey day yankin Birtaniya na ketare Akrotiri da Dhekelia, da Yammacin Kogin Jordan (West Bank). Haka kuma an ruwaito wasu ayyuka a Azerbaijan.

0 comments: