Tsohon kwamandan sojojin Serb na Bosnia, Ratko Mladic, wanda aka samu da laifin kisan kare dangi da laifukan yaki da kuma laifukan cin zarafin bil’adama, ya rasu yana da shekaru 83.
Rahotanni sun ce Mladic ya rasu ne a wani asibitin kurkukun Majalisar Dinkin Duniya (UN) da ke birnin Hague na ƙasar Netherlands. Gidan talabijin na Serbia da na Serb na Bosnia sun bayar da rahoton rasuwar, yayin da wani jami’in Majalisar Dinkin Duniya ya tabbatar da ita.
An yanke wa Mladic hukuncin daurin rai da rai a shekarar 2017, bayan an same shi da hannu a wasu munanan laifuka da aka aikata a lokacin yakin Bosnia na shekarar 1992 zuwa 1995.
An same shi da laifin kisan kare dangi saboda rawar da ya taka a kisan kiyashin Srebrenica na shekarar 1995, inda aka kashe sama da Musulman Bosnia 8,000, musamman maza da yara maza.
Mladic, wanda aka fi sani da “Mahaucin Bosnia”, ya shafe shekarun ƙarshe na rayuwarsa a gidan yari bayan kotun ƙasa da ƙasa ta same shi da alhakin wasu daga cikin manyan laifukan cin zarafin bil’adama da aka aikata a Turai tun bayan Yaƙin Duniya na Biyu.
Rasuwarsa ta kawo ƙarshen rayuwar ɗaya daga cikin fitattun mutanen da aka gurfanar a gaban kotun ƙasa da ƙasa bisa zargin aikata manyan laifukan yaki a Bosnia.

0 Comment about the Post: