Thursday, July 9, 2026

Ƙasashen Sahel Sun Samu Sabon Tabbaci Na Goyon Bayan Soja Daga Rasha.

Ƙasashen Sahel Sun Samu Sabon Tabbaci Na Goyon Bayan Soja Daga Rasha.

Ƙasar Rasha ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da bai wa gwamnatocin mulkin soja na Burkina Faso da Mali da Nijar cikakken goyon bayan soja domin ƙarfafa yaƙinsu da ƙungiyoyi masu tayar da ƙayar baya a yankin Sahel.

Sanarwar ta fito ne bayan wani babban taro da Ministan Harkokin Wajen Rasha, Sergei Lavrov, ya yi da ministocin harkokin wajen ƙasashen uku a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar.

A cikin sanarwar haɗin gwiwa, Rasha ta ce za ta ci gaba da taimakawa wajen inganta ƙwarewa da ƙarfin rundunonin sojin ƙasashen mambobin Ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Sahel (AES).

Burkina Faso da Mali da Nijar na ƙarƙashin gwamnatocin soja ne bayan juyin mulki da aka yi tsakanin shekarun 2020 zuwa 2023. Tun daga lokacin ne suka rage alaƙarsu da Faransa tare da ƙara kusanci da Rasha a fannin tsaro da diflomasiyya.

Baya ga tallafin soja, Rasha na kuma ƙoƙarin faɗaɗa haɗin gwiwa da ƙasashen AES a fannonin makamashi da hakar ma'adinai.

Taron na Yamai ya biyo bayan irin makamancin taron da aka gudanar a birnin Moscow a watan Afrilun shekarar 2025, inda bangarorin suka tattauna hanyoyin ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarsu.

0 Comment about the Post: