Monday, July 6, 2026

Adadin waɗanda suka mutu sakamakon girgizar ƙasa a Venezuela ya kai 3,535, yayin da dubban mutane har yanzu ba su da matsuguni.

Adadin waɗanda suka mutu sakamakon girgizar ƙasa a Venezuela ya kai 3,535, yayin da dubban mutane har yanzu ba su da matsuguni.

Adadin mutanen da suka rasu sakamakon mummunar girgizar ƙasa biyu da ta afku a ƙasar Venezuela ya ƙaru zuwa mutum 3,535, kamar yadda hukumomin ƙasar suka sanar. Har yanzu dubban mutane na ci gaba da zama ba tare da matsuguni ba fiye da mako guda bayan aukuwar ibtila'in.

Hukumomi sun bayyana cewa mutane 16,740 ne suka jikkata, yayin da mutum 17,854 suka rasa gidajensu bayan girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 7.2 da 7.5 da ta auku a ranar 24 ga Yuni, cikin tazara ta 'yan daƙiƙu kaɗan.

Mafi yawan barnar ta shafi birnin Caracas da jihar gabar teku ta La Guaira, inda jami'an ceto da na agaji ke ci gaba da gudanar da ayyukansu. 
Gwamnatin Venezuela ta ce sama da mutum 12,800 na zaune a sansanonin wucin gadi guda 80 da aka tanada domin waɗanda bala'in ya shafa.

Shugabar ƙasa mai riƙon ƙwarya, Delcy Rodríguez, ta kare matakan da gwamnati ta ɗauka bayan girgizar ƙasar, tana mai cewa an tura jami'an tsaro cikin gaggawa domin gudanar da ayyukan ceto. 
Ta kuma sanar da shirin kafa sabon rundunar soji ta musamman domin taimakawa wajen tunkarar bala'o'in gaggawa a nan gaba.

A jihar La Guaira, ana ci gaba da jana'izar waɗanda suka mutu, yayin da jami'an binciken gawarwaki ke jigilar gawawwaki zuwa makabarta, tare da binne waɗanda ba a tantance asalinsu ba.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa tana faɗaɗa ayyukan jin kai tare da haɗin gwiwar gwamnatin Venezuela. 
Kakakin majalisar, Stéphane Dujarric, ya ce ƙungiyoyin ceto da injiniyoyi da ma'aikatan lafiya na ci gaba da aiki a yankunan da bala'in ya fi shafa, yayin da ake kammala cikakken nazarin bukatun waɗanda abin ya shafa domin ƙara inganta ayyukan agaji.

Girgizar ƙasar ta kasance ɗaya daga cikin mafi muni da Venezuela ta fuskanta cikin shekaru da dama, inda ta yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyi tare da barin dubban iyalai cikin matsanancin buƙatar matsuguni da kulawar lafiya da tallafin jin kai.

0 Comment about the Post: