Mahukuntan ƙasar Iran sun sanar da jadawalin jana'iza da binne marigayi Ali Khamenei, tsohon Jagoran Addini na kasar, wanda ya rasu a wani harin sama da Amurka da Isra'ila suka kai a farkon wannan shekara.
Kafafen yada labaran gwamnatin Iran sun bayyana cewa za a fara gudanar da jana'izarsa a birnin Tehran ranar 4 ga Yuli, sannan a ci gaba da bukukuwan makoki a birnin Qom ranar 7 ga Yuli.
Daga bisani za a binne shi a garinsu na haihuwa, Mashhad, ranar 9 ga Yuli.
Tun da farko an shirya binne Khamenei a watan Maris, amma aka dage saboda rikicin da ya barke tsakanin Iran da Amurka da Isra'ila.
Khamenei, mai shekaru 86 a duniya, ya jagoranci Iran tun daga shekarar 1989 bayan rasuwar Ruhollah Khomeini, wanda ya jagoranci juyin juya halin Musulunci a kasar. A tsawon mulkinsa, ya taka muhimmiyar rawa wajen gina da kuma karfafa hukumomin siyasa da na tsaro na Iran.
Magajinsa, Mojtaba Khamenei, bai cika bayyana a bainar jama'a ba tun bayan fara yakin Amurka da Isra'ila da Iran. Sai dai kwanan nan, Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, ya ce Mojtaba Khamenei na taka muhimmiyar rawa wajen tafiyar da harkokin gwamnati yayin da ake ci gaba da tattaunawar diflomasiyya tsakanin Iran da Amurka bayan yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma a watan Afrilu.
Ana sa ran jana'izar za ta samu halartar dubban masu makoki da jami'an gwamnati da manyan baki daga kasashen waje, a wani muhimmin lamari a tarihin siyasar Iran.

0 Comment about the Post: