Saturday, June 27, 2026

Amurka da Iran Sun Yi Musayar Hare-Hare, Lamarin da ke Barazanar Durƙushewar Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta tsakaninsu

Amurka da Iran Sun Yi Musayar Hare-Hare, Lamarin da ke Barazanar Durƙushewar Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta tsakaninsu

Ƙasashen Iran da Amurka sun yi musayar hare-hare a yankin Tekun Fasha, lamarin da ya ƙara fargabar cewa yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakanin ƙasashen biyu na iya rushewa.

Rundunar juyin juya halin Musulunci ta Iran (IRGC) ta ce a ranar Asabar ta kai hari kan wuraren sojojin Amurka a yankin Tekun Fasha, a matsayin martani ga hare-haren Amurka kan wuraren ajiye makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa da na’urorin gano hari na Iran.

Amurka ta ce hare-haren nata sun kasance martani ne ga abin da ta kira harin jirgi mara matuƙa da Iran ta kai kan wani jirgin ruwa na kasuwanci a mashigin Hormuz.

Rundunar Sojojin Amurka a yankin (CENTCOM) ta bayyana cewa ta kai hari kan wuraren adana makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa na Iran, tare da wasu wuraren gano bayanan sirri a bakin teku.

Kafofin watsa labaran Iran sun ruwaito cewa an samu fashewa a kusa da tashar Taheroui da ke birnin Sirik a kudancin Iran, amma jami’ai sun ce tashar tana aiki yadda ya kamata kuma ba a samu babbar asara ba.

Shugaban Amurka Donald Trump ya zargi Iran da karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta bayan rahoton harin jirgi mara matuƙa kan jirgin kasuwanci, yayin da Mataimakin Shugaban Amurka JD Vance ya yi gargadin cewa duk wani sabon hari zai fuskanci martani.

IRGC ta kuma yi gargadin cewa idan aka sake kai hari, martanin Iran zai fi girma.

Tashin Hankali Tsakanin Iran da Bahrain

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta ce ta kai hari kan wuraren da ke da alaƙa da sojojin Amurka ne bayan hare-haren Amurka a kudancin Iran.

Bayan haka, Bahrain ta zargi Iran da kai hare-haren jirage marasa matuƙa a ƙasarta, tana mai cewa hakan keta huruminta ne da kuma dokokin ƙasa da ƙasa.

Bahrain ta ce tana da haƙƙin kare tsaron ƙasarta.

Haka kuma, hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ruwa ta Birtaniya ta ce wani jirgin ruwa ya samu hari da wani abu da ba a san asalinsa ba a mashigin ruwan Hormuz. 
An lalata wani ɓangare na jirgin, amma dukkan ma’aikatan jirgin suna cikin aminci.

Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Na Cikin Hatsari

Sabbin rikice-rikicen sun jefa shakku kan makomar yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka da Iran suka cimma a ranar 17 ga Yuni.

Bangarorin biyu na zargin juna da karya yarjejeniyar, wadda aka tsara domin buɗe hanyar tattaunawa kan batutuwa da suka haɗa da zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigin Hormuz.

Batun Makaman Nukiliya

Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA), Rafael Grossi, ya ce duk wata yarjejeniya ta ƙarshe tsakanin Amurka da Iran dole ta ƙunshi tsauraran matakan sa ido domin tabbatar da cewa Iran ba ta ƙera makaman nukiliya ba.

Iran ta ce ba ta da niyyar ƙera makaman nukiliya, amma masu sa ido na ƙasa da ƙasa na neman damar bincika wuraren nukiliyar ƙasar domin tabbatar da hakan.

0 Comment about the Post: