Akalla mutane 18, ciki har da mata da yara, suka rasa rayukansu bayan wata babbar mota da ke dauke da ‘yan gudun hijirar Afghanistan da suka dawo daga Pakistan ta kife a wata babbar hanya a gabashin Afghanistan.
Hatsarin ya faru ne da sanyin safiya a gundumar Qarghayi da ke lardin Laghman, lokacin da motar ta kauce hanya ta fada cikin rami. Rahotanni daga hukumomi sun ce motar na dauke da iyalai da kayayyakinsu yayin da suke kan hanyarsu zuwa Kabul, babban birnin Afghanistan.
Jami’an yankin sun bayyana cewa ana kyautata zaton direban motar ya yi barci ne a kan hanya kafin motar ta kwace mashi. Fiye da mutane 30 sun jikkata a hatsarin, wasu daga cikinsu na cikin mawuyacin hali, kuma an garzaya da su zuwa asibitoci domin samun kulawa ta gaggawa.
Rahotanni sun tabbatar da cewa akalla yara 10 ne suka mutu a cikin wadanda suka rasa rayukansu.
An kai wadanda suka jikkata zuwa asibitoci a lardin Nangarhar, makwabta, inda wasu ke ci gaba da karbar kulawa ta musamman.
Hukumomin gwamnatin wucin gadi sun mika ta’aziyya ga iyalan wadanda abin ya shafa tare da sanar da bayar da tallafin gaggawa ga wadanda suka tsira da kuma iyalan wadanda suka rasu.
Hadurran mota suna yawan faruwa a Afghanistan saboda lalacewar hanyoyi da rashin ingancin motoci da kuma raunin aiwatar da dokokin tuki.
Matsalar ta kara tsananta sakamakon yawan mutanen da ke komawa gida daga kasashen waje, inda ake tilasta musu yin tafiya cikin motocin kaya da suka cika fiye da kima.
Rahotanni daga Majalisar Dinkin Duniya sun nuna cewa dubban daruruwan ‘yan Afghanistan sun koma daga Pakistan a bana, lamarin da ke kara matsin lamba kan hanyoyin sufuri da hidimomin agaji.
Hukumomi sun yi gargadi cewa idan ba a inganta hanyoyi da tsarin sufuri ba, irin wadannan mummunan hadurra na iya ci gaba da faruwa yayin da iyalai ke kokarin komawa gida cikin yanayi mai hatsari.

0 Comment about the Post: