Tuesday, July 7, 2026

Ƙasar Amurka Ta Kaddamar da Hare-haren Sama Kan Iran Kan Zargin Kai Hari Ga Jiragen Ruwa na Kasuwanci.

Ƙasar Amurka Ta Kaddamar da Hare-haren Sama Kan Iran Kan Zargin Kai Hari Ga Jiragen Ruwa na Kasuwanci.

Sojojin Amurka sun kaddamar da jerin hare-haren sama kan wasu wurare a Iran bayan zargin cewa Iran ta kai hare-hare kan jiragen kasuwanci uku da ke bi ta mashigar ruwan Hormuz, a cewar Rundunar Tsakiyar Sojin Amurka (CENTCOM).

A cikin wata sanarwa da ta fitar, CENTCOM ta ce an kaddamar da hare-haren ne domin dorawa Iran "babban farashi" saboda abin da ta bayyana a matsayin kai hare-hare kan jiragen kasuwanci da ke amfani da daya daga cikin manyan hanyoyin jigilar kayayyaki na duniya.

Sanarwar ta kara da cewa hare-haren da ake zargin Iran ta kai ba su da wani dalili, suna da hadari, kuma sun saba da yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

Rahotannin kafafen yada labaran Iran sun ce akalla makamai masu linzami shida sun fada a yankin tashar jiragen ruwa ta Taheroui da ke garin Sirik a kudancin Iran. Sai dai hukumomin Iran ba su bayyana adadin wadanda suka mutu ko suka jikkata ba, ko kuma irin barnar da aka yi.

A bangaren Amurka kuwa, jami'an soji ba su bayyana takamaiman wuraren da aka kai wa harin ba.

Wannan shi ne karo na farko da aka san Amurka ta kai hari kai tsaye kan Iran tun bayan musayar hare-haren da kasashen biyu suka yi a karshen watan da ya gabata.

Lamarin ya kara tayar da hankalin kasashen duniya, yayin da ake fargabar sabon rikicin zai iya kara dagula tsaro a yankin Gabas ta Tsakiya tare da shafar zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar ruwan Hormuz.

0 Comment about the Post: