Wednesday, July 30, 2025

Tarihin fir'auna da Annabi Musa (AS)

 

Tarihin fir'auna da Annabi Musa (AS)

Fir'auna Sunan wani sarki ne da ya mulki bani israi'la bisa zulunci Wanda sai da Allah ya aiko masa da manzonsa Annabi Musa (AS) domin yayi mashi wa'azi da gargadi a bisa zulunci da kafircin da yake aikatawa a bayan kasa. Fir'auna ya rayu ne a kasar misra wato kasar Egypt.

Sunan fir'auna suna ne na sarauta da ake Kiran duk wani sarki da ya mulki kasar ta misra a wancan lokacin, saboda Sunan fir'auna na gaskiya shine Walid bn Musab.

Hakika duk musulmi yasan Sunan fir'auna domin sai da Allah madaukakin sarki ya ambace shi a cikin Alkur'ani sau 74 a wurere daban-daban.

Fir'auna ya kasance Azzalumin sarki Mai girman Kai da nuna dagawa Allah madaukakin sarki, baya ga Azabtar da kabilar bani israi'la da yayi na tsayon shekaru ya  Kuma karkashe masu 'ya'yayensu jarirai bisa zulunci da fargaban kada a haifi Annabi Musa (AS) Wanda bokayensa suka bashi labarin cewa shine zai kawo karshen mulkinsa a doron kasa.

Bayan sanun labarin cewa za'a haifi wani yaro Wanda shine zai kawo karshen mulkin zaluncinsa, Fir'auna yasa a rinka kashe duk wani yaro da aka haifa a misra, an ce sai da ya kashe jarirai sama da dubu Arba'in duk a kokarinsa na wanzuwar Annabi Musa (AS)......

A dan dakace mu Zamu cigaba.


SHARE THIS

Author:

I am a personal blogger by experience, interesting in creativity, learning new things and sharing Islamic contents for the benefit of Muslim ummah.

0 comments: