An zaɓi Dakta A’isha Mustapha a matsayin sabuwar Shugabar Ƙungiyar Likitocin Nijeriya (NMA), reshen Jihar Kaduna, bayan gudanar da zaɓen ƙungiyar a makon da ya gabata.
Dakta A’isha ƙwararriyar likita ce a fannin mata da haihuwa (Obstetrics and Gynaecology), kuma ta samu nasarori da dama a fannin aikin likita, ilimi da hidimar kiwon lafiya.
Kafin samun wannan matsayi, Dakta A’isha ta samu lambobin yabo da karramawa daban-daban, ciki har da karramawa daga Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, a wajen ƙaddamar da shirin PECCIN Launch 2025.
A shekarar 2024, ta kuma samu Certificate of Excellence in Peer Reviewing daga Global Academy Publisher, yayin da a shekarar 2023 ta samu Impact Award daga Ovarian Cancer Coalition.
A fannin ilimi, Dakta A’isha ta yi fice sosai. A shekarar 2015, ta zama ɗalibar da ta fi ƙwarewa a jarabawar WACS Part I a fannin Obstetrics and Gynaecology. Haka kuma, ɗaliban likitanci na Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, sun ba ta lambar yabo ta Mafi hazakar Malama a shekarun 2016 da 2017.
Ta kuma kammala karatunta a matsayin mafi hazakar ɗaliba a fannin Obstetrics and Gynaecology a Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, a shekarar 2008.
A matsayinta na sabuwar shugabar NMA ta Kaduna, Dakta A’isha ta ce za ta mayar da hankali wajen kare haƙƙin likitoci, tabbatar da aiwatar da albashi da alawus-alawus na CONMESS, inganta walwalar likitoci da samar da tallafin lafiyar ƙwaƙwalwa.
Ta kuma bayyana cewa za ta yi aiki wajen inganta inshorar lafiya, lokutan aiki, kariyar shari’a ga likitoci da samar da ƙarin damar horaswa da bunƙasa ƙwarewar ma’aikatan lafiya.
Dakta A’isha, wadda ’yar asalin Jihar Kano ce, ta yi makarantar firamare a Hotoro, sannan ta halarci Federal Government College Kano kafin ta shiga Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.
A halin yanzu tana aiki a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello (ABUTH), Shika, kuma ta halarci ƙasashe daban-daban domin ƙarin ilimi da ƙwarewa.
Kafin zaɓenta a matsayin shugabar NMA Kaduna, ta taɓa zama shugabar Ƙungiyar Likitoci Mata ta Nijeriya, reshen Kaduna, sannan ta riƙe muƙamin Sakatariyar NMA ta Jihar Kaduna.
Dakta A’isha ta gode wa abokan aikinta bisa amincewar da suka nuna mata, tare da yin alƙawarin shugabanci cikin gaskiya, adalci da rashin nuna bambanci.
Ta kuma yi kira ga likitoci da su haɗa kai domin ci gaban ƙungiyar da kuma inganta harkokin kiwon lafiya a Jihar Kaduna da Nijeriya baki ɗaya.
