Rahotanni sun bayyana cewa hare-haren da Isra’ila ta kai a yankin Gaza sun yi sanadin mutuwar akalla mutum 11 a cikin rana guda, ciki har da yara biyu.
Majiyoyin lafiya a Gaza sun ce an kai hare-haren ne ta sama da kuma luguden wuta a wasu yankuna daban-daban, wanda ya haddasa asarar rayuka da jikkata wasu da dama. An kuma ce gidaje da wasu muhimman wurare sun lalace sakamakon harin.
Shaidun gani da ido sun bayyana cewa hare-haren sun jefa al’ummar yankin cikin firgici, yayin da iyalai ke kokarin tsira da rayukansu tare da neman mafaka.
Har yanzu dai babu cikakken bayani daga bangaren Isra’ila dangane da wannan hari, amma ana ci gaba da samun tashin hankali a yankin Gaza.
Kungiyoyin kare hakkin bil’adama na ci gaba da kira da a tsagaita wuta tare da kare rayukan fararen hula, musamman yara, yayin da rikicin ke kara kamari.
Tags
Labaran Duniya
